Gwamna Inuwa Yahaya Ya Halacci Taron NEC, Ya Jaddada Goyon Bayansa Ga Tsarin 'Renewed Hope' Na Shugaba Tinubu


Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, ya halarci babban taron Majalisar Tattalin Arziki ta Kasa (NEC) wanda aka gudanar a Abuja. Taron, wanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya jagoranta tare da Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima, ya mayar da hankali ne kan sabon tsarin ci gaban kasa na shekarar 2026 zuwa 2030 mai taken "Samar da Ci Gaba Mai Dorewa da Zai Dama da Kowa."


Yayin taron, Shugaba Tinubu ya bayyana kudurinsa na daidaita tattalin arziki da inganta rayuwar al'umma ta hanyar zuba jari a fannin ilimi da more rayuwa. Shi ma a nasa bangaren, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana cewa Jihar Gombe tana sahun gaba wajen marawa wadannan kudurori baya ta hanyar sauya fasalin fannin noma, ilimi, da masana'antu.



Gwamnan ya jaddada cewa Jihar Gombe ta zama zakaran gwajin dafi a Arewa Maso Gabas wajen samar da ayyukan yi da wadatar abinci, sannan ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da aiki kafada-da-kafada da gwamnatin tarayya domin samar wa talaka romon damokradiyya.